Sarkin musulmi ya sanar da ganin watan Sallah a Najeriya
Gobe Juma’a ce ranar Idin Sallah karama.
Muhammad Sa’ad Abubakar III, Sarkin Musulmin Najeriya.
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya.
Hakan ya tabbatar da ranar Juma’a, 1 ga watan Shawwal ta shekarar 1444 Bayan Hijira a matsayin ranar Idin Sallah karama.
Sarkin, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (NSCIA) ya ce an tabbatar da sahihancin ganin watan a wurare da dama a fadin kasar.
Ya bukaci musulmi da su ci gaba da kasancewa jakadu na zaman lafiya da kowa ba tare da nuna wani bambanci a tsakanin al’umma ba.
Ya yi addu’ar Allah Ya yi riko da hannayen sabbin shugabanni Ya kuma albarkaci kasar baki daya.