Satar shadda yadi 3 ta kai matashi gidan yari a Kano

Wata kotun Musulinci a Kano ta tsare wani matashi mai shekaru 30 a gidan kaso bisa tuhumar sa da satar shadda yadi uku.

Satar shadda yadi 3 ta kai matashi gidan yari a Kano

Kotu

Wata kotun Musulinci a Kano ta tsare wani matashi mai shekaru 30 a gidan kaso bisa tuhumar sa da satar shadda yadi uku.

’Yan sanda ne dai suka gurfanar mutumin wanda ke zaune a unguwar Tudun Murtala a gaban kotun bisa zargin sa da kuruciyar bera da kuma shiga wuri ba da izini ba.

Tun da fari dai, dan sanda mai gabatar da kara, Abdul Wada ya shaida wa kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin ne a ranar 18 ga watan Yuli a unguwar Danbare da ke jihar, da misalin karfe 10:30 na dare.

Ya bayyana cewa wanda ake zargin ya balle shagon wani mai suna Abdulkadir Ibrahim, ya saci wani buhun Leda da yadin ke ciki.

Laifin dai ya saba wa sashi na 133 da na 201 na kundin Dokar Kotin Shari’ar Musulinci.

Alkalin kotun, Mai Shari’a Alhaji Isma’il Muhammad, ya dage zaman kotun zuwa ranar 3 ga watan Agusta, domin ci gaba da sauraron karar.

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha

NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana

Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba

An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka