Saudiyya ta zartar wa dan kasarta hukuncin kisa kan ta’addanci

An zartar wa al-Asmari hukuncin kisa kan laifin kafa kungiyar ta’addanci

Saudiyya ta zartar wa dan kasarta hukuncin kisa kan ta’addanci

Tutar kasar Saudiyya

Gwamnatin Saudiyya ta zartar da hukuncin kisa ga wani dan kasar da kotu ta kama da laifin kafawa da kuma jagorantar kungiyar ta’addanci da kuma kulla kawance da wasu kungiyoyin ta’addanci da nufin kai hare-hare a cikin kasar.

Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Saudiyya ta ce an zartar wa mutumin mai suna Yasser bin Mohammed al-Asmari hukuncin kisa ne a ranar Litinin bayan kotunan kasar sun tabbatar da hukuncin a kansa.

Ma’aikatar ta bayyana cewa laifukan al-Asmari sun hada da “kafa kuniygar ta’addanci da nufin kai hare-hare musamman ga jami’an tsaro a cikin kasar Saudia.”

“Ya kuma yi mubaya’a ga jagoran wata kungiyar,”  ta’addanci sannan ya kulla kawance da wasu kungiyoyin ta’addanci inda ya bukaci taimakonsu, in ji sanarwar ma’aiakatar.

An kuma sami al-Asmari da laifin bayar da mafaka ga masu tsattsauran ra’ayi da kuma daukar su aiki da kuma ba su horo a kan hada abubuwan fashewa, gami da ba su umarnin inda za su kai hare-hare.

Ma’aikatar ta ce al-Asmari ya kuma dauki makami a yankunan da ke fama da rikici, tare da bukatar ‘yan dabarsa da su same shi a can.

Baffa Bichi da Barau Jibrin sun gana a Abuja

MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP

Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo