Sheikh Yasser Dossary ya dawo limanci a Masallacin Harami

Sheikh Sudais ya sanar da dawowar Sheikh Yasir Ad Dawsary limanci a Masallacin Harami da wasu limamai biyu a Masallacin Madina

Sheikh Yasser Dossary ya dawo limanci a Masallacin Harami

Yasser Dossary

Babban Limamin Masallatan Harami Sheikh Abdul Rahman al-Sudais, ya sanar da dawowar Sheikh Yasser Dossary da wasu limamai biyu.

Sheikh Sudai ya sanar cewa Sheikh Yasir zai ci gaba da limanci a Masallacin Harami da ke Makkah.

Sauran limamn biyu, Sheikh Khalid Muhanna da kuma Sheikh Ahmad Hudhaify, za su ci gaba da limanci ne a Masallacin Manzon Allah Sallal Lahu Alaihi Wa Sallama da ke Madina.

Sheikh Sudai, ya roki Allah “Ya yi musu jagora Ya ba su dacewa a cikin limancinsu ga al’ummar Musulmi,” in ji sanarwar da Hukumar Gudanarwar Masallatai Masu Alfarma ta fitar.

Wannan albishir daga Sheikh Sudais ya zo ne a daidai lokacin da ake shirin fara azumin watan Ramadan na bana.

A baya dai ana fargabar malaman ba za su yi limanci ba a watan Ramadan, saboda karewar wa’adin kwantiraginsu na shekara huɗu a masallacin.

Da haka adadin limaman masallacin Harami zai sake komawa 8 kamar haka:

1- Sheikh Abdur Rahman As Sudais

2- Sheikh Abdullah Awad Al Juhany

3 – Sheikh Maher Al Muaiqly

4- Sheikh Bandar Baleelah

5- Sheikh Faisal Ghazzawi

6- Sheikh Saleh Al Humaid

7- Sheikh Usaamah Khayyat

8- Sheikh Yasser Dossary

Shekarar 2015 Sheikh Dawsary ya fara limancin sallar Taraweeh a Masallacin Harami a matsayin bakon liman, kafin shekarar 2019 Masarautar Saudiyya ta nada shi a matsayin cikakken limami, wanda za a rika sabunta kwangilarsa bayan shekara hudu.

Zaɓen Edo: Yadda aka kama masu sayen ƙuri’a da ’yan daba

Sarakunan Nijar sun kai wa Gwamnatin Yobe ziyarar jaje

Ɗan majalisa ya yi jinjina kan naɗa Danyaya Sarkin Ningi

’Yan Sanda sun kama gungun ’yan fashi 7 a Katsina