Shekarau ya fice daga PDP
Tsohon Gwamnan Jihar Kano Malam Ibrahim Shekarau ya bayyana ficewarsa daga Jam’iyyar PDP, kamar yadda mai magana da yawunsa, Malam Sule Ya’u Sule ya sanar. Sule ya bayyana cewa mai gidansa Malam Shekarau ya fice daga PDP ne saboda zargin rashin adalci da uwar Jam’iyyar PDP ta masa. Tun bayan da uwar jam’iyyar ta rushe […]

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Malam Ibrahim Shekarau ya bayyana ficewarsa daga Jam’iyyar PDP, kamar yadda mai magana da yawunsa, Malam Sule Ya’u Sule ya sanar.
Sule ya bayyana cewa mai gidansa Malam Shekarau ya fice daga PDP ne saboda zargin rashin adalci da uwar Jam’iyyar PDP ta masa.
Tun bayan da uwar jam’iyyar ta rushe shugabannin jam’iyyar PDP na Kano, da kuma yadda ake ta samun rade-radin cewa za a ba Kwankwasiyya shugabancin ne ake fara samun matsala.