Shekarau ya saya fom din tsayawa takarar sanata
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya saya fom din tsayawa takarar kujerar sanata ta Kano ta Tsakiya. Malam Shekarau, wanda tsohon Minsitan Ilimi ne a zamanin mulkin Jonathan, kwanan nan ya fice daga Jam’iyyar PDP, inda ya koma Jam’iyyar APC. Ita dai kujerar sanatan Kano ta Tsakiya, a yanzu haka Sanata Kwankwaso ne […]

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya saya fom din tsayawa takarar kujerar sanata ta Kano ta Tsakiya.
Malam Shekarau, wanda tsohon Minsitan Ilimi ne a zamanin mulkin Jonathan, kwanan nan ya fice daga Jam’iyyar PDP, inda ya koma Jam’iyyar APC.
Ita dai kujerar sanatan Kano ta Tsakiya, a yanzu haka Sanata Kwankwaso ne ke rike da ita, sannan kuma a kwanakin baya, an ruwaito cewa Sanata Lado ne zai tsaya takarar kujerar.