Shugaban APC ya shiga bayan labule da gwamnonin jam’iyyar

Taron na sirri na gudana a shelkwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Shugaban APC ya shiga bayan labule da gwamnonin jam’iyyar

Gwamnonin APC na wata ganawa da shugaban jam’iyyar, Sanata Abdullahi Adamu gabanin zaben gwamnoni da na ’yan majalisar dokoki da ke tafe a ranar Asabar.

Dukkan mambobin Kwamitin Zartaswa na jam’iyyar na halartar taron na sirri da ke gudana a shelkwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Yawancin gwamnonin jam’iyyar ta APC na neman yin tazarce a zaben da ke tafe a ranar Asabar, yayin da kuma wasunsu sun sha kaye ko kuma sun samu nasarar zama zababbun Sanatoci a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu.

Sakataren jam’iyyar APC na Kasa, Iyiola Omisore; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa kuma dan takarar gwamnan Jihar Delta a jam’iyyar, Sanata Ovie Omo-Agege; Dan takarar gwamnan APC a Jihar Ribas, Tonye Cole; Abubakar Sadiq, tsohon hafsan hafsoshin sojin sama, wanda shi ne dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Bauchi, na daga cikin wadanda suka halarci taron.

Haka kuma, gwamnonin jihohin Kebbi Atiku Bagudu da na Jigawa Abubakar Badaru da kuma na Zamfara na cikin wadanda ke halartar zaman.

An sanya dokar hana fita a wasu yankunan Taraba

Jami’an NSCDC sun daƙile harin ’yan bindiga a Kano

Matsalar Tsaro: Ku sayi makamai don kare kanku — Sarkin Argungun

Mai juna biyu na wata 8 ta shigar da ƙarar neman saki