Shugabannin ECOWAS na ganawa a Abuja

Ana sa ran bayan kammala taron, ECOWAS za ta fitar da sabon shugabanta.

Shugabannin ECOWAS na ganawa a Abuja

Shugabannin ƙasashen da ke ƙarƙashin ƙungiyar ECOWAS da wakilansu na ganawa a Cibiyar Taro ta Fadar Gwamnatin Tarayya da ke Abuja.

Wannan taron shi ne taro na 65 na shugabannin ƙasashen ECOWAS.

Ana sa ran shugabannin ECOWAS, za su sanar da sabon shugaban ƙungiyar wanda zai jagorancenta na tsawon shekara guda.

Amma hakan zai tabbata ne kawai a ƙarshen taron, wanda aka fara da misalin ƙarfe 12 na rana.

A lokacin shugabancin Bola Ahmed Tinubu a matsayin Shugaban ECOWAS, an fuskanci juyin mulki a wasu ƙasashen mambobin ƙungiyar.

Hakan ya sanya ECOWAS ƙoƙarin ci gaba da dawo da Nijar, Mali, da Burkina Faso cikin ƙungiyar, bayan a baya sun bayyana ficewarsu daga cikinta.

Duk da ƙoƙarin ECOWAS, ƙasashen sun sake jaddada ƙudurinsu na ficewa daga cikinta.

Idan ba a manta ba, ƙasashe irin su Nijar, Burkina Faso da Mali sun fuskanci juyin mulki daga sojoji, waɗanda suka hamɓarar da gwamnatin fararen hula a ƙasashen.

Hakan ne ya sanya ECOWAS yin barazanar ɗaukar matakin soji musammam a Nijar matuƙar sojoji ba dawo da mulkin demokuraɗiyya a ƙasar ba.

’Yan sanda sun ƙwace sakamakon zaɓe a Ribas

Yadda mutanen Jigawa suka ƙi fita zaɓen ƙananan hukumomi 

Za mu yi wa Kwankwaso ritaya a 2027 — Doguwa

’Yan daba sun ƙone ofishin hukumar zaɓen Akwa Ibom