Sojin Larabawa sun kakkabo jiragen ’yan Houthi a Saudiyya

Sun tarwatsa jiragen mayakan Houthi makare da ababen fashewa a Bahar Maliya.

Sojin Larabawa sun kakkabo jiragen ’yan Houthi a Saudiyya

Kakakin Rundunar Kawancen Kasashen Larabawa, Kanar Turki Al-Maliki

Rundunar kawancen kasashen Larabawa da Saudiyya ke jagoranta sun baro jiragen yaki marasa matuka na ’yan tawayen Houthi na kasar Yemen.

Rundunar ta kama jiragen ne makare da ababen fashewa a yankin Kudancin Saudiyya ta kuma ta tarwatsa su.

Kakakin Rundunar, Kanar Turki Al-Maliki ya ce: “A safiyar Alhamis rundunar ta cafke jirage mara matuki dauke da makamai da ’yan tawayen Houthi suka kai wa fararen hula hari da su a yankin Kudanci”.

Harin na zuwa ne bayan a ranar Laraba sojin ruwan rundunar kawancen sun tarwatsa wasu jiragen ruwan mayakan Houthi makare da ababen fashewa a kan tekun Bahar Maliya.

A baya-bayan nan ’yan tawayen na Yemen sun tsananta kai hare-hare a makwabtan kasar sabanin dokokin kasashen duniya da ma na cikin gidan Yemen din.

Boko Haram sun ƙone makarantu a Borno

Har yanzu ’yan bindiga ba su saki matar Manjo Janar Rabe ba

An binne gawar Manjo Janar Rabe a Katsina

Wasu tsiraru ne ke rura matsalar tsaro a Najeriya — Christopher Musa