Sojoji sun cafke wadanda suka kai hari Cocin Owo

Manjo-Janar Lucky Irabor ya ce sojoji sun kama maharan tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro.

Sojoji sun cafke wadanda suka kai hari Cocin Owo

Sabon Hafsan Hafsoshin Najeriya, Manjo-Janar LEO Irabor

Hedikwatar Tsaro ta Kasa (DHQ) ta bayyana cewar ta yi nasarar cafke maharan da suka kai harin cocin Katolika da ke garin Owo a Jihar Ondo.

Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Najeriya, Manjo-Janar Lucky Irabor ne ya bayyana hakan a yayin wani taron tattaunawa da shugabannin kafafen yada labarai a hedikwatar tsaron da ke Abuja.

Manjo-Janar Irabor ya ce sojoji sun kama ababen zargin ne tare da hadin gwiwar wasu hukumomin tsaro.

A ranar Lahadi 5 ga watan Yuni ne wasu ’yan bindiga suka dira cocin St. Francis Xavier da ke garin Owo a jihar Ondo dake Kudu maso Yammacin Najeriya.

Ba su bata lokaci ba suka buda wuta kan masu ibada inda suka kashe mutum 40 tare d jikkata wasu da dama.

Wannan lamari ya tayar ya yamutsa hazo a tsakanin mabiya addinai, inda kowane bangare ke tayar da jijiyoyin wuya a kokarin kare addininsa.

An ceto wani yaro da aka sace, an kama mutum 4 Gombe

Fursunoni 52 sun zana jarabawar kammala sakandare a Kano

Mutum 18 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Neja

Amurka ta janye sojojinta daga Najeriya