Sojoji sun ceto ma’aikaciyar agaji daga hannun ISWAP bayan shekara 4

Sojojin Najeriya sun ceto wata ma’aikaciyar agaji Grace Taku, bayan ta ta shafe shekara hudu a hannun mayakan kungiyar ISWAP.

Sojoji sun ceto ma’aikaciyar agaji daga hannun ISWAP bayan shekara 4

Sojojin Najeriya sun ceto wata ma’aikaciyar agaji Grace Taku, bayan ta ta shafe shekara hudu a hannun mayakan kungiyar ISWAP.

A safiyar Asabar wata majiyar tsaro ta shaida mana cewa ana duba lafiyar Grace a asibitin sojoji na Maimalari da ke Maiduguri, bayan an ceto ta.

Majiyar ta ce sojojin sun “An ceto ta a galabaice, amma cikin hankalinta,” a wani samame a maboyar mayakan ISWAP.

Grace, ma’aikaciyar kungiar agaji ta Action Against Hunger (ACH)ce, kuma wata abokiyar aikinta ta tabbatar wa wakilinmu cewa sun kai mata ziyara a asibitin sojojin.

Jami’ar ta ce,  “Mun ji dadin ganin ta bayan shekara uku da wata 10 a hannun ISWAP. Na yi kuka sosai da na gan ta. Allah mai iko!

“Mun samu labari cewa sojoji sun ceto ne a 13 ga watan Mayu, 2023, Allah Ya saka wa sojojin rundunar Operation Hadin Kai da alheri.”

Wata majiyar ta ce kungiyar ISWAP ta sayar da Grace a matsayin baiwa, bayan rashin daidaitawa a tattaunawar kungiyar da Gwamnatin Tarayya a 2021.

A watan Yulin 2019 ne mayakan ISWAP suka yi garkuwa da Grace Taku da abokan aikinta biyar a yankin Damasak na Jihar Borno.

Kungiyar ta kashe sauran ta abokan aikin Grace su biyar, domin nuna fushinsu kan rashin samun biyan bukatunta daga gwamnati da jami’an tsaro.

Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N825 a Legas

Na gaji bashin 8.9bn a matsayin shugaban APC — Ganduje

Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC ba