Sojoji sun ceto mutum 9 daga hannun ‘yan bindiga a Kaduna 

Sun kuma yi nasarar kwato shanu 90 da aka sace.

Sojoji sun ceto mutum 9 daga hannun ‘yan bindiga a Kaduna 

Sojojin Nijar

Dakarun rundunar ‘Operation Forest Sanity’ ta Sojin Kasa na Najeriya sun ceto wasu mutum tara da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Jihar Kaduna.

Dakarun sun samu nasarar kubutar da mutanen ne yayin wani samame da suka maboyar ‘yan bindigar da ke garin Kaso a Karamar Hukumar Chikun ta jihar.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya ce sojojin sun yi artabu da ‘yan bindigar ne a babban titin Tantatu, lamarin da ya sa suka tsere cikin dajin.

A sanarwar da ya fitar a ranar Litinin, Aruwan ya ce Sojojin sun yi bincike a sansanin tare da ceto mutum tara da suka yi garkuwa da su.

“Sojojin sun kuma kwato shanu 90 da ‘yan bindigar da suka gudu suka bari wadanda za a mika su ga Hukumar Kula da Kiwon Dabobbi ta Jihar Kaduna domin tantance su,” in ji shi.

Ya ce an gudanar da wani samamen sirri a tsaunin Bawa Rikasa, inda aka samu nasarar kwato babura hudu a hannun barayin daji.

Aruwan, ya ce mutum tara da aka ceto za a tantance su kafin a sake sada su da iyalansu.