Sojoji sun dakile sabon hari a Madagali
A yau Talata rundunar sojojin Najeriya ta yi nasarar dakile wani mummunan hari da ‘yan Boko Haram ta kintsa kaiwa garin Madagali a jihar Adamawa. Mataimakin Daraktan hulda da jama’a na runduna ta 7 Kanal Ado Isa ne ya fitar da sanarwar, ya ce rundunar ta kashe maharan da dama tare da kwace makaman su, […]
A yau Talata rundunar sojojin Najeriya ta yi nasarar dakile wani mummunan hari da ‘yan Boko Haram ta kintsa kaiwa garin Madagali a jihar Adamawa.
Mataimakin Daraktan hulda da jama’a na runduna ta 7 Kanal Ado Isa ne ya fitar da sanarwar, ya ce rundunar ta kashe maharan da dama tare da kwace makaman su, lokacin da su ka yi yunkurin kaiwa sansanin sojojin hari.