Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina
Gwamnatin ta ce dakarun sun samu bayanan sirri wanda suka kai ga kashe ‘yan fashin.
Gwamnatin Jihar Katsina, ta ce dakarun sojin Najeriya sun kashe ’yan fashi bakwai a jihar.
Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na jihar, Nasir Mu’azu ne, ya shaida wa manema labarai a ranar Juma’a.
- Yadda na tsira a hatsarin jirgin ruwan Goronyo — Hakimi
- Ɗaliba ta rasu a ƙoƙarin duba sakamakon jarabawarta
Ya ce sojojin sun kuma ƙwace babura huɗu a Karamar Hukumar Kankara.
Ya ce samamen ya ɗauki sama da awa biyu a ranar Alhamis, bayan samun bayanan sirri cewa ’yan fashin sun kai hari ƙauyen Baba.
Wannan lamari ya faru ne kwanaki kaɗan bayan wani hari da ’yan fashi suka kai wani masallaci.
Harin ya yi sanadin salwantar rayukan sama da mutane 30, rahotanni kuma na cewa adadin ya kai kusan 50.