Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina

Gwamnatin ta ce dakarun sun samu bayanan sirri wanda suka kai ga kashe ‘yan fashin.

Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina, ta ce dakarun sojin Najeriya sun kashe ’yan fashi bakwai a jihar.

Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na jihar, Nasir Mu’azu ne, ya shaida wa manema labarai a ranar Juma’a.

Ya ce sojojin sun kuma ƙwace babura huɗu a Karamar Hukumar Kankara.

Ya ce samamen ya ɗauki sama da awa biyu a ranar Alhamis, bayan samun bayanan sirri cewa ’yan fashin sun kai hari ƙauyen Baba.

Wannan lamari ya faru ne kwanaki kaɗan bayan wani hari da ’yan fashi suka kai  wani masallaci.

Harin ya yi sanadin salwantar rayukan sama da mutane 30, rahotanni kuma na cewa adadin ya kai kusan 50.

KADVS ta daƙile yunƙurin sace yara da ceto wasu a Zariya

Gwamnatin Tinubu na yunƙurin hana ni yin takara — Peter Obi

An gurfanar da ƙarin mutum 17 bisa zarginsu a kisan malama

An kama matashi ɗauke da hannun mutum da bindigogi