Sojoji sun tarwatsa sansanin ‘yan Boko Haram a Ngwuri Gana
Rundunar sojin saman Najeriya NAF ta ce, jirgin yakin saman sojoji a shirinsu na Operation Lafiya Dole da suka yi ranar 5 ga Nuwamba 2018 sun tarwatsa sansanin ‘yan Boko Haram tare da raunata maharan a Ngwuri Gana da ke Borno. Rundanar ta ce, sansanin wata moboya ce da ‘yan Boko Haram ke shirya kaiwa […]
Jirgin Sojin Saman Najeriya
Rundunar sojin saman Najeriya NAF ta ce, jirgin yakin saman sojoji a shirinsu na Operation Lafiya Dole da suka yi ranar 5 ga Nuwamba 2018 sun tarwatsa sansanin ‘yan Boko Haram tare da raunata maharan a Ngwuri Gana da ke Borno.
Rundanar ta ce, sansanin wata moboya ce da ‘yan Boko Haram ke shirya kaiwa jama’a hari a yankunan da ke garin Kumshe.
Kakakin rundunar Eya Kwamanda Ibikunle Daramola, ya tabbatar da aukuwar hakan ya kara da cewa, sansanin na daya daga cikin maboyar Boko Haram.