Sojojin Amurka sun kai hare-hare ta sama a Syria

Amurka ta ce wannan mataki da ta dauka ba shi da nasaba da Isra’ila.

Sojojin Amurka sun kai hare-hare ta sama a Syria

Sojojin Amurka sun ce sun kai hare-hare ta sama wurare biyu da sojin juyin-juya-hali na Iran ke amfani da su a Syria.

A wata sanarwa da Sakataren Tsaron Amurka ya fitar Lloyd Austin, ya bayyana hare-haren na tsantsar kare kai.

Lloyd Austin ya ce martani ne ga jerin hare-haren da kungiyoyin da ke samun goyon bayan Iran suka fara kai wa dakarunta tun daga ranar 17 ga wannan wata na Oktoba.

Sun ce martani ne kan hare-haren da suke addabar sojin Amurka da ke Iraqi da Syria hare-hare.

Sama da mako guda da rabi kenan da sojin Amurka ke zafafa kai hare-hare kan kungiyar masu dauke da makamai da Iran ke marawa baya.

Ma’aikatar Tsaro ta Pentagon ta ce an kai wa kawancen da Amurka ke jagoranta a Iraqi da Syria hari sama da sau 16 cikin wannan watan.

Sanarwar ta ce sai da ta aike da sako ga shugaban addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei a game da hare-haren da ake kai wa dakarun kasar a Gabas Ta Tsakiya a daidai lokacin da ake zaman dar-dar a yankin Gabas ta Tsakiya saboda yakin Isra’ila a Gaza.

Amurka ta ce wannan mataki da ta dauka a kan Iran da kungiyoyin da take mara wa baya a Syria ba shi da nasaba da Isra’ila, hasali ma ba ta tuntubi Isra’ilar ba kafin daukar sa.

Zaɓen Edo: Yadda aka kama masu sayen ƙuri’a da ’yan daba

Sarakunan Nijar sun kai wa Gwamnatin Yobe ziyarar jaje

Ɗan majalisa ya yi jinjina kan naɗa Danyaya Sarkin Ningi

’Yan Sanda sun kama gungun ’yan fashi 7 a Katsina