Sojojin Chadi sun kashe ’yan Boko Haram 207
Rundunar sojojin kasar Chadi ta fitar da sanarwa cewa ta kashe ’yan Boko Haram 207 a wani kauyen Najeriya da ke iyaka da kasar Kamaru da kuma Chadi. Rundunar sojojin ta fitar da sanarwar ne a ranar Talatar da ta gabata.Sanarwar ta bayyana a lokacin bata-kashi tsakanin sojojinta da ’yan Boko Haram a kauyen Garambu […]
Rundunar sojojin kasar Chadi ta fitar da sanarwa cewa ta kashe ’yan Boko Haram 207 a wani kauyen Najeriya da ke iyaka da kasar Kamaru da kuma Chadi.
Rundunar sojojin ta fitar da sanarwar ne a ranar Talatar da ta gabata.
Sanarwar ta bayyana a lokacin bata-kashi tsakanin sojojinta da ’yan Boko Haram a kauyen Garambu sojan kasarta daya ne ya rasa ransa, inda tara suka samu raunika.
Har zuwa yanzu ba a tabbatar da sahihin labarin ba duk da cewa rundunar kasar ta bayyana ta kwato wadansu kananan makamai da harsasai da kuma motaci biyu a hannun mayakan Boko Haram din.
Idan ba a manta ba kasar Nijar da Kamaru da Chadi sun hada gwiwa wajen taimaka wa Najeriya don a dakile ayyukan Boko Haram, inda a watan jiya ne kasar Chadi tare da taimakon Kamaru ta girke sojojinta don fatattakar Boko Haram da ke yunkurin shiga kasarta.
A watan jiya ne dai kungiyar Hadin kan Afirka ta amince a samar da sojojin hadin gwiwa, sannan ta bukaci majalisar dinkin duniya ta amince a kaddamar da hare-haren a kan ’yan Boko Haram.