Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa 240 sun jikkata 650 a Gaza

Hukumoni a Zirin Gaza sun ce Falasdinawa 240 Isra’ila a kashe, ta kuma jikkata wasu 650 daga ranar Juma’a.

Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa 240 sun jikkata 650 a Gaza

Gawarwakin yaran wani Bafalasdine Abu Quta a harin da sojojin Isra’ila suka kai garin Rafah da ke Kudancin Zirin Gaza, a yayin janai’zarsu ranar 8 ga Oktoba, 2023 bayan kasamin fada tsakanin Hamas da Isra’ila. (Hoto: SAID KHATIB / AFP)

Hukumoni a Zirin Gaza sun ce Falasdinawa 240 Isra’ila a kashe, ta kuma jikkata wasu 650 daga ranar Juma’a.

Hukumar Hamas ta ce Isra’ila ta kai hare-hare sama da 400 da jirage da kuma ta kasa a sassan Gaza tun bayan karewar wa’adin tsagaita wuta da bangarorin suka yi.

Hamas ta ce sojojin Isra’aila sun tsananta hare-hare a sassan yankin Khan Younis da ke Kudancin Zirin Gaza inda suka rika rusa gidaje da mutane a cikinsu.

Tun bayan karewar wa’adin yarjejeniyar tsagaita wutan mako guda da Hamas da Isra’ila suka cim-ma, sojojin Isra’ila suka rika ragargazar yankunan Gaza.

Akasarin wadanda hare-haren Isra’ila yi ajalinsu a Gaza dai kananan yara ne da tsofaffi da kuma mata.

A kimanin wata biyu da Isra’ila ke ragargazar Gaza, yawan Falasdinawan da ta kashe sun haura mutum dubu 15.