Surukin Sarkin Musulmi ya rasu a Landan

Marigayin ya yi gamo da ajalinsa bayan ’yar takaitacciyar jinya a birnin Landan.

Surukin Sarkin Musulmi ya rasu a Landan

Muhammad Sa’ad Abubakar III, Sarkin Musulmin Najeriya.

Sultan na Sakkwato, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar da Sarkin Bichi na Jihar Kano, Alhaji Nasiru Ado Bayero sun yi rashin surukinsu, Abubakar Imam Galadanchi.

Abubakar Imam Galadanchi ya rasu ne bayan ’yar takaitacciyar jinya a birnin Landan da ke Birtaniya.

Jami’in hulda da jama’a na Fadar Sarkin Musulmi, Aminu Halliru ne ya tabbatar da hakan yayin zantawarsa da wakilinmu.

A cewarsa, Sarkin Musulmi da kuma Sarkin Bichi na auren ’ya’yan marigayin wanda mai yankan kauna ta debewa tsammani.

An kama ɗan sandan ƙarya a Kano

Zargin kwartanci: Hisbah ta kama kwamishina da matar aure a Jigawa

Fashewar tankar mai: Mamata sun ƙaru zuwa 170

Alabshin N14m ba ya isa ta —Sanata Kalu