Tashin Dala: Gwamnan CBN ya sauka kawai —PDP
Farashin Dala yan ninka sau uku a shubabancin Emefiele a CBN.
Godwin Emefiele, Gwamnan Babban Bakin Najeriya (CBN).
Jam’iyyar PDP ta bukaci Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele ya sauka daga mukaminsa saboda tashin gwauron zabon farashin Dala da kuma lalacewar tsare-tsaren kudade a Najeriya.
Sakataren Yada Labaran PDP, Kola Olagbondiyan, ya ce shugabancin Emefiele a CBN, a karkashin gwamnatin jam’iyyar APC shi ne lokacin da tsarin kudaden Najeriya ya fi shiga mawuyacin hali har farashin Dala ya ninku fiye da sau uku.
- Kudaden shiga daga bangaren man fetur sun ja baya
- Ba za mu fallasa masu taimakon ’yan ta’adda ba —Gwamnati
- ’Yan bindiga daga Zamfara da Katsina sun fara kai hari Kano
Ologbondiyan ya ce, “Ya kamata a tuna cewa lokacin da aka nada Emefiele a matsayin Gwamnan CBN a 2014 farashin cajin Dala N164 ne.
“Amma zwau yanzu da CBN a karkashin Emefiele da gwamnain APC, farashin Dala ya kusa kaiwa N600, lamarin da ke neman durkusar da tattalin arzikin Najeriya.
“Abin takaicin shi ne shugabancin Emefiele a CBN ya gaza a babban aikinsa na gudanar da tsare-tsaren tattalin arziki, amma yake ta yada farfaganda sabanin abin da ke faruwa a zahiri a bangaren na tattalin arziki,” inji shi.