Tinubu na ganawa da Akpabio da Jonathan a Aso Rock

A tattaunawar har da Ganduje da Uzodinma

Tinubu na ganawa da Akpabio da Jonathan a Aso Rock

Tinubu

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yanzu haka yana ganawa sabon Shugaban Majalisar Dattajai, Godswill Akpabio, a fadarsa ta Aso Rock da ke Abuja.

Kazalika, cikin tattaunawar akwai Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma da tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

Shi ma Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu na tare da su a tattaunawar.

Gabanin haka, Shugaba Tinubu ya kuma gana da tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan a ofishinsa.

Sai dai har yanzu babu cikakken bayani game da makasudin duka ganawar tasu.

Shi ma shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya gana da Tinubun.

Gwamnatin Tinubu na yunƙurin hana ni yin takara — Peter Obi

An gurfanar da ƙarin mutum 17 bisa zarginsu a kisan malama

An kama matashi ɗauke da hannun mutum da bindigogi

NDLEA ta kama miyagun ƙwayoyi tan 3.9 da kama mutum 599