Tinubu ya janye nadin da ya yi wa matashi mai shekara 24 a shugabancin FERMA

Nadin matashin dai ya janyo ce-ce-ku-ce a fadin Najeriya

Tinubu ya janye nadin da ya yi wa matashi mai shekara 24 a shugabancin FERMA

Imam Kashim Imam

Shugaban Kasa Boa Tinubu, ya bayar da umarnin janye sunan Injiniya Imam Kashim Imam daga nadin da ya yi masa a matsayin shugaban Majalisar Daraktocin Hukumar Gyaran Hanyoyi ta Tarayya (FERMA).

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Ajuri Ngelale ya fitar da maraicen Alhamis.

“Umarnin janye sunan zai fara aiki ne nan take. Sai dai duk sauran nade-naden da aka yi na hukumar gudanarwar hukumar ta FERMA na nan daram,” in ji sanarwar.

Nadin matashin dai shekara 24 a makon da ya gabata ya janyo ce-ce-ku-ce matuka a fadin Najeriya.

Yayin da wasu suke jinjina masa kan nada matasa, wasu kuma sun soki lamirinsa kan nada wanda sam ba shi da wata kwarewa ya jagoranci hukumar.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan