Tinubu ya yi sauye-sauye a Jami’ar Abuja

A baya naɗin Aisha ya janyo ce-ce-ku-ce, inda wasu ke ganin ba ta cancanci riƙe muƙamin ba.

Tinubu ya yi sauye-sauye a Jami’ar Abuja

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya sauke Aisha Maikudi daga muƙaminta na Shugabar Jami’ar Abuja, wadda yanzu ake kira da Jami’ar Yakubu Gowon.

Sanarwar sauke Maikudi ta fito ne jim kaɗan bayan ta jagoranci bikin maraba da sabbin ɗalibai a jami’ar.

Tun farko, naɗinta ya jawo ce-ce-ku-ce, inda wasu malaman jami’ar suka ce ba ta cancanta ta riƙe wannan matsayi bisa doka.

Tinubu ya naɗa Farfesa Lar Patricia Manko a matsayin Muƙaddashiyar Shugabar Jami’ar na tsawon watanni shida.

Sai dai ba za ta iya neman kujerar dindindin ba idan aka buɗe damar neman muƙamin.

 

Cikakken bayani na tafe…

Sojoji sun daƙile harin Boko Haram, sun ceto mutum 9 a Borno

’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 3 a Binuwai

Mahara sun sace bsarake, sun harbi matarsa a ƙauyen Ondo

Sarkin Musulmi ya umarci a fara neman jinjirin watan Muharram