Tinubu zai yi wa ’yan Najeriya jawabi da daddare

Zai yi jawabin ne da karfe 7 na yamma

Tinubu zai yi wa ’yan Najeriya jawabi da daddare

Tinubu

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu zai yi wa ’yan Najeriya jawabi da yammacin Litinin.

Mai magana da yawun shugaban, Dele Alake ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da safiyar Litinin.

Ya ce shugaban zai yi jawabin ne da misalin karfe 7:00 na maraice, kodayake babu karin bayani a kan musabbabin jawabin nasa.

Sanarwar ta bukaci kafafen yada labarai su jona da gidan talabijin na kasa (NTA) da gidan rediyon Najeriya domin watsa jawabin kai tsaye.

Tags