Tinubu zai ziyarci Katsina

Tinubu zai ƙaddamar da wasu ayyukan Gwamna Umar Dikko Radda

Tinubu zai ziyarci Katsina

Karon farko tun bayan zamowarsa shugaban ƙasa, Bola Tinubu zai ziyarci Jihar Katsina.

Kwamishinan yaɗa labaran jihar, Bala Zango, ne ya shaida wa manema labarai hakan a ranar Laraba.

Sanarwar ta ce shugaban zai kai ziyarar ce, domin ƙaddamarwa da kuma rangadin wasu ayyukan da Gwamna Umar Dikko Radda ya aiwatar a jihar.

Karin bayani na tafe.