Kasashen Waje

Kasashen Waje

An ji ƙarar harbe-harbe a kusa da Fadar Shugaban Guinea

An fara jin harbe-harben ne da ƙarfe 9 na safiyar Talata, daga nan aka ci gaba da luguden wutar harsasai har tsawon sa’a guda.

ISIS ta kashe mutum 31, wasu 169 sun jikkata a masallacin Juma’a a Pakistan 

Harin shi ne mafi muni a babban birnin Pakistan tun harin bom da ya lalata otel ɗin Marriott a 2008.

Za a soma bai wa raƙuma fasfo a ƙasar Saudiyya

A shekarar 2024, gwamnatin Saudiyya ta ƙiyasta cewa akwai kusan raƙuma miliyan biyu da dubu dari biyu a ƙasar.

An kashe ɗan marigayi Gaddafi a Libya

Wasu ’yan bindiga su kimanin mutum huɗu sun harbe shi ne a gidansa da ke birnin Zintan.

Harin ’yan ta’adda ya hallaka direbobin tanka 15 a Mali

Mali na fama da matsalar tsaro tun 2012, sakamakon hare-haren ‘yan ta’adda masu alaƙa da Al-Qaeda da ISIS, da kuma ‘yan bindiga.