Trump ya ce zai bar Sadik Khan ya je Amurka 1

Shugaban Amurka Barack Obama ya shirya kai ziyara garin Hiroshima da ke kasar Japan, wanda  wannan shi ne karon farko da wani  shugaban Amurka  zai kai ziyara  garin, wurin da Amurka ta jefa  wa makamin kare dangi a watan Agustan shekarar 1945 lokacin Yakin Duniya na Biyu, inda ya kashe mutane akalla dubu 129.Tsawon shekaru […]

Trump ya ce zai bar Sadik Khan ya je Amurka 1
Trump ya ce zai bar Sadik Khan ya je Amurka 1

Shugaban Amurka Barack Obama ya shirya kai ziyara garin Hiroshima da ke kasar Japan, wanda  wannan shi ne karon farko da wani  shugaban Amurka  zai kai ziyara  garin, wurin da Amurka ta jefa  wa makamin kare dangi a watan Agustan shekarar 1945 lokacin Yakin Duniya na Biyu, inda ya kashe mutane akalla dubu 129.
Tsawon shekaru 70 da suka gabata, kusan ko wane  shugaban Amurka yana  kauracewa ziyarar  wadannan wuraren biyu  da Amurka ta yi wa barna, wato garuruwan Hiroshima da Nagasaki.
Fadar White House ta ce Shugaba Obama zai  ziyarci Hiroshima bisa rakiyar Firaministan Japan Shinzo Abe  a ranar 21 zuwa 28 ga wannan watan, lokacin da zai kai  ziyara  a kasashen bietnam da kuma Japan.
Mataimakin Mai Bai wa  Shugaba  Obama  Shawara kan Harkokin Tsaro, Ben Rhodes, ya ce  ba ya tsammanin cewa  shugaba Obama zai roki  gafarar wannan harin bam din da aka  kai  Hiroshima da Nagasaki ba.
Ya ce  “ko kusa  Shugaba Obama ba zai sake  duba  wannan batun harin bam da  aka a Hiroshima ba a karshen Yakin Duniya na Biyu, maimako  zai  duba  gaba ne  domin abin da zai ciyar da kasashen biyu gaba.”
Ziyarar ta zo dai-dai da lokacin da aka kwashe  shekaru 75 bayan Tokyo ta kai harin ba-zata ga sojojin Amurka da ke gabar tekun Jihar Hawaii. Kodayake, kasashen biyu sun zamo manyan kawayen juna bayan Yakin Duniya na Biyu.
Shugaba Obama zai tafi  kasar ne da zummar ya gana da  shugabannin kungiyar kasashen nan Bakwai da  Suka Fi Kowa  Arziki a Duniya. Kuma daya daga cikin dalilan ziyartarsa  Hiroshima shi ne ya kara jadda da kudirinsa  na ganin cewa gwamnatin Amurka  ta ci  gaba da ba da gudunmuwarta ga harkokin  tsaro a duniya, domin ci  gaba da  samun kyakkyawar  tsaro  a kowane kusurwa ta duniya.
Ko cikin watan da ya gabata sai da Sakataren Harkokin Wajen Amurka, John Kerry, ya kai  ziyara Hiroshiman, inda  ya ce ziyararsa tamkar sharar fage ce ta jaddada wa  duniya cewa Amurka tana nan, tana iyaka  bakin  kokarinta  na ganin cewa duniya  ta kaucewa barazanar makamin Nukiliya  daga  wasu  kasashen duniya.