Tsohon ɗan majalisa ya mutu yayin kallon wasan Najeriya da Afrika ta Kudu

Tsohon ɗan Majalisar Tarayyar, Cairo Ojougboh ya mutu sakamakon bugun zuciya yayin kallon wasan Najeriya da Afrika ta Kudu.

Tsohon ɗan majalisa ya mutu yayin kallon wasan Najeriya da Afrika ta Kudu

Tsohon ɗan Majalisar Tarayya daga jihar Delta, Cairo Ojougboh ya mutu sakamakon bugun zuciya yayin kallon wasan Najeriya da Afrika ta Kudu.

Cairo Ojougboh ya yanke jiki ya mutu ne a daidai lokacin da za a yi bugun daga kai sai mai tsaron rago a wasan hamayya a gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON).

Marigayin ya kasance dan jam’iyyar APC ne kuma mai yawan babatu a kan batutuwan da suka taso a zauren majalisa.

Wasan Najeriya da Afrika ta Kudu, wanda a karshe Najeriya ta yi nasara, ya yi zafi sosai, kuma ya tayar da kura a soshiyal midiya.

NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa

An ƙaddamar wa ’yan kasuwa sabon tsarin biyan haraji a Gombe

Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya

Malamai sun fara yajin aiki a Ebonyi