Tsohon Shugaban kungiyar direbobi na Jihar Oyo ya shiga hannu
Rundunar ’yan sandar Jihar Legas ta kama tsohon Shugaban kungiyar Direbobi ta NURTW a jihar Oyo, Alhaji Mukaila Lamidi, wanda aka fi sani da suna Audiliary, rundunar ta kame shi ne bayan da wani dillalin makamai ba bisa ka’ida ba, ya shiga hannunta, wanda ya ce shugaban na NURTW na cikin sahun masu saye daga […]
Rundunar ’yan sandar Jihar Legas ta kama tsohon Shugaban kungiyar Direbobi ta NURTW a jihar Oyo, Alhaji Mukaila Lamidi, wanda aka fi sani da suna Audiliary, rundunar ta kame shi ne bayan da wani dillalin makamai ba bisa ka’ida ba, ya shiga hannunta, wanda ya ce shugaban na NURTW na cikin sahun masu saye daga hannunsa, kuma ya sayar masa da bindigogi biyu, babba da karama,samfurin AK47 da 9MM da 9MMdubu 360.
Da aka gabatar da shi gaban manema labarai domin karyata ko gaskata sayen wadannan bindigogi, tsohon shugaban kungiyar direbobin, ya ce ba shakka ya sayi bindigogi, kuma ba ya saya ne da niyyar aikata ayyukan assha da su ba ne, sai domin ya kare kansa.
Ya ce wani abokinsa ne ya gabatar da mai sayar da wadannan bindigogin gare shi, domin ya fada cewa shekaru uku da suka gabata wasu mutane sun taba shiga gidansa da niyyar kashe shi, amma ba su kashe shi ba, sai suka kashe babban dansa, shi kuma suka ji masa ciwo a kafa, wanda ya nuna muna, inda ya ce tun daga lokacin ne ya ga akwai bukatar ya mallaki bindigogi domin gudun bacin rana.
Ya kuma tabbatar da cewa an sayar masa bindigogin a kan Naira dubu 350.
…Gwamnan Oyo ya yaba wa ’yan sanda kan kamun
Kabir Yayo Ali, Daga Ibadan
Gwamnan Jihar Oyo, Sanata Abiola Ajimobi, ya jinjina wa ’yan sanda da suka kama tsohon shugaban bangaren kungiyar direbobi (NURTW) na jihar, Alhaji Mukaila Lamidi da ake yi wa lakabi da ‘Audiliary’, wanda ake zargin bangarensa da bangaren Lateef Oloruntoki, mai lakabin Tokyo da hannu wajen kashe Malam Bala Usman Shanono, shugaban kungiyar dalibai, sashen kiwon lafiya na Jami’ar Ahmadu Bello, cikin watan Yunin shekarar 2011 a Ibadan.
A wancan lokaci ne Rundunar ‘yan sanda ta Jihar Oyo ta yi alkawarin bayar da kyautar Naira dubu dari biyar ga dukkan wanda ya ba ta labarin maboyar wadannan shugabanni biyu da ake nemansu ruwa a jallo, domin tuhumarsu da laifin kisan gilla a dalilin barkewar tarzoma a tsakanin magoya bayansu da ta yi sanadin mutuwar Bala Usman Shanono da wasu mutane masu yawan.
Jinjinar dai tana cikin wata takardar sanarwa da mai ba shi shawara na musamman a kan kafofin labarai, Dokta Festus Adedayo ya sanya wa hannu, inda Gwamna Abiola ya ce, “’Yan sandan da suka kamo wannan mutum sun cancanci yabo kuma akwai alamar samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar”.