Uba Sani ya mayar wa iyalan Abacha filayen da El-Rufai ya ƙwace musu
Lauyan iyalan Abacha, Reuben Atabo, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai.

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani (Hoto: Gwamnatin Kaduna)
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya mayar wa iyalan Tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Sani Abacha, filayensu guda biyu da tsohon jihar, Nasir El-Rufai ya ƙwace a lokacin mulkinsa.
Lauyan iyalan Abacha, Reuben Atabo, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai.
- SON ta gargadi masana’antu kan bi ka’idoji wajen sarrafa kayayyaki
- Gwamnatin Jigawa ta bankado ma’aikatan bogi 6,348
A cewar sanarwar da Babban Daraktan Ma’aikatar Kula da Filaye ta Jihar Kaduna, Mustapha Haruna ya fitar, Gwamna Uba Sani ya aike wa iyalan Abacha wasiƙa.
A wasiƙar, an tabbatar da mayar musu da filayen sannan an buƙaci su biya harajin da aka saba karɓa sakamakon mallakar filayen.
Tsohon Gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, ya ƙwace filayen ne a ranar 28 ga watan Afrilun 2022.
Bayan ƙwace filayen, ya sanar da matakin nasa a cikin jaridu tare da soke
Sai dai matakin na El-Rufai ya haifar da cece-kuce, inda wasu ke ganin tsohon gwamnan bai kyauta ba.