WAEC ta sanar da ranar fara jarrabawar WASSCE ta 2021

Za a fara jarrabawar ne ranar Litinin, 16 ga watan Agustan 2021.

WAEC ta sanar da ranar fara jarrabawar WASSCE ta 2021

Wasu dalibai na rubuta jarrabawa

Hukumar Shirya Jarrabawar ta Afirka ta Yamma (WAEC) ta sanar da ranar Litinin, 16 ga watan Agustan 2021 a matsayin ranar da za a fara rubuta jarrabawar kammala sakandire (WASSCE).

Babban jami’in hukumar a Najeriya, Mista Patrick Areghan ne ya sanar da haka a Legas ranar Talata.

A cewar sanarwar, “La’akari da jadawalin da aka amince da shi na kasa da kasa, jarrabawar WASCCE ta shekarar 2021 a dukkan yankin da ake rubutata za ta gudana daga ranar Litinin 16 ga watan Agusta zuwa Juma’a, takwas ga watan Oktoban 2021.

“To sai dai a Najeriya, za a kammala jarrabawar ne ranar 30 ga watan Satumban 2021, bayan an shafe makonni bakwai kenan ana yinta,” inji sanarwar.

A baya dai, akan rubuta jarrabawar ne a tsakanin watannin Afrilu da Mayun kowacce shekara, in ban da a bana da aka sami tsaiko sakamakon yadda annobar COVID-19 ta kawo dagula lamura.