WAEC za ta fitar da sakamakon SSCE na 2020 a makon gobe

WAEC ta dage ranar fitar da sakamakon jarabawar sakandare na 2020

WAEC za ta fitar da sakamakon SSCE na 2020 a makon gobe

Hukumar Shirya Jarabawa ta Yammacin Afirkta (WAEC) ta dage ranar fitar da sakamakon jarabawarta na kammala sakandare da aka gudanar bana zuwa mako mai zuwa.

A ranar Laraba 28 ga Oktoboa ya kamata WAEC ta fitar da sakamakon jarabawar amma ta ce ta dage saboda rikici da kone-konen da aka yi a boren #EndSARS a sassan Najeriya.

“A yau Hukumar ta shirya fitar da sakamakon jarabawar amma dokar hana fita da aka sanya a makon jiya ya sa aka dage fitar da sakamakon zuwa makon gobe. Nan gaba za a sanar da ainihin ranar”, inji sanarwar da WAEC ta wallafa a shafinta na Twitter.

Jami’in Hulda ja Jama’a na Ofishin Hukumar a Najeriya, Demianus Ojijeogu, ya tabbatar da hakan.

Idan ba a manta ba bullar annobar COVID-19 da dokar kulle da aka sanya domin dakile yaduwarta ta sanya an daga gudanar da jarabawar a Najeriya da wasu kasashe.

A baya an saba gudanar da jarabawar ne tsakanin watan Mayu da Yuni, amma bullar a annobar ta sa a 2020 aka gudanar a watan Agusta.

Boko Haram sun ƙone makarantu a Borno

Har yanzu ’yan bindiga ba su saki matar Manjo Janar Rabe ba

An binne gawar Manjo Janar Rabe a Katsina

Wasu tsiraru ne ke rura matsalar tsaro a Najeriya — Christopher Musa