Wanda ya yi tattaki daga Legas don Buhari ya nesanta kansa da hotunan kalanda

Sulaiman Hashim, matashin da ya yi tattaki daga Legas zuwa Abuja a kafa don murnar nasarar Janar Muhammadu Buhari a zaben Shugaban kasa, ya nesanta kansa da wasu hotuna da ake bugawa a kalanda da ke nuna shi a cikin daula. Sulaiman wanda ya bayyana korafin a yayin zantawa da Aminiya a shekaranjiya Laraba, ya […]

Wanda ya yi tattaki daga Legas don Buhari ya nesanta kansa da hotunan kalanda
Wanda ya yi tattaki daga Legas don Buhari ya nesanta kansa da hotunan kalanda

Sulaiman Hashim, matashin da ya yi tattaki daga Legas zuwa Abuja a kafa don murnar nasarar Janar Muhammadu Buhari a zaben Shugaban kasa, ya nesanta kansa da wasu hotuna da ake bugawa a kalanda da ke nuna shi a cikin daula. Sulaiman wanda ya bayyana korafin a yayin zantawa da Aminiya a shekaranjiya Laraba, ya ce ana hada hotunan ne ta hanyar amfani da na’urar kwamfuta a sanya fuskarsa ko daukacin jikinsa a kan wasu hotunan na daban da ba ya da alaka da su.

Ya ce hotunan sun hada da wadanda ake nuna shi a tsakanin wani namiji da mace da aka bayyana su a matsayin iyayensa. Sauran hotunan inji shi sun hada da na wani kayataccen gida da ke da motoci shida a harabarsa wanda aka ce mallakarsa ne a birnin Abuja. Ya ce a kullum yana samun kiraye-kiraye a waya daga wurare daban-daban na kasar nan a kan al’amari, “Wannan karairayi da suke ta yadawa a kaina na taka muhimmiyar rawa wajen samar da karin masu tattaki irin nawa, wanda a kullum sai karuwa suke yi,” inji Sulaiman.