Wasu ’yan siyasa na kokarin shirya wa gwamnatin Tinubu mummunar zanga-zanga – DSS

DSS ta ce ta gano mutanen kuma tana sanya musu ido

Wasu ’yan siyasa na kokarin shirya wa gwamnatin Tinubu mummunar zanga-zanga – DSS

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu

Hukumar tsaro ta DSS ta ce ta gano shirin da wasu ’yan siyasa ke yi na shirya wa Shugaban Kasa Bola Tinubu mummunar zanga-zanga.

DSS, wacce ba ta bayyana sunan mutanen ba, ta ce suna kokarin yin amfani da kungiyoyin dalibai da na kabilu da na matasa wajen cim ma burin nasu.

A cewar hukumar, ana son shirya zanga-zangar ce domin a nuna gazawar Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro a kan abin da suka bayyana da manufofin tattalin arziki.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwar da Kakakin hukumar, Peter Afunanya ya fitar a ranar Litinin.

Sanarwar ta ce tana ankarar da jama’a ne bisa bayanan sirrin da ta samu.

Sai dai ta ce tuni ta gano masu kokarin kitsa zanga-zangar, kuma tana nan tana zuba musu ido.

Daga nan sai DSS ta yi kira ga manyan makarantu da su ja kunnen dalibansa da kada su kuskura a yi amfani da su wajen yi wa zaman lafiyar kasa zagon kasa.

Zaɓen Edo: An fara ƙirga ƙuri’u

Zaɓen Edo: INEC ta tsawaita kaɗa ƙuri’a a wasu yankuna

’Yan sanda sun kama mai yi wa ’yan bindiga safarar makamai a Kaduna

Gwamnan Kano ya raba wa makarantu kujeru da tebura 73,000