Wata mata ta cire wa kishiyarta kunne da cizo

Wata mata ta yago kunnen kishiyarta da cizo a yayin fadan da ya kaure tsakaninsu a kan dan daya daga cikinsu. Kishiyoyin masu suna Rabi da Zubaida sun yi ta ba wa hammata iska ne a gidan mijinsu da ake kira Dan Borno, a Unguwar Zai, da ke karamar hukumar Dutse a jihar Jigawa. Fada […]

Wata mata ta cire wa kishiyarta kunne da cizo

Wata mata ta yago kunnen kishiyarta da cizo a yayin fadan da ya kaure tsakaninsu a kan dan daya daga cikinsu.

Kishiyoyin masu suna Rabi da Zubaida sun yi ta ba wa hammata iska ne a gidan mijinsu da ake kira Dan Borno, a Unguwar Zai, da ke karamar hukumar Dutse a jihar Jigawa.

Fada ya fara kaurewa tsakanin Zubaida da Rabi har suka yi ta bugun juna ne bayan dan Rabi ya zuba ruwa a cikin tankin injin din Zubaida, saboda ta zage shi.

Ana cikin dauki ba dadin ne Zubaida, wadda aka zuba wa injinta ruwa, ta gantsara wa Rabi cizo a kunne, sai da ta yago rabin kunnen.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar jigawa, SP Abdu Jinjiri, ya ce Zubaida da Rabi sun amsa tambayoyi kafin a ba da belinsu a caji ofis na karamar hukumar Dutse.

SP Jinjiri ya kara da cewa da zarar ’yan sanda sun kammala bincike a kan al’amarin za a gurfanar da matan a gaban kotu domin su girbi abin da suka shuka.

Wani makwabcin gidan Dan Borno a Unguwar Zai ya shaida wa Aminiya cewa Zubaida da Rabi sun dade suna zaman doya da manja da fada a kan ’ya’ya, har ta kai ’ya’yan daya ba sa zuwa kofar dakin daya saboda tsananin kishi.

A wasu lokauta akan samu matan da kan jikkata abokan zamansu ko ma su yi yunkurin hallaka su ba don komai ba sai don tsananin kishi.

Sojoji Sun Kashe ’Yan Boko Haram 23 A Borno

Fasinjoji sun jikkata yayin da tankar mai ta yi bindiga a Abuja

PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen Edo, za ta garzaya kotu

1.5bn kaɗai aka sanya a asusunmu — Tsohon Kwamishinan Sakkwato