Wutar Lantarki ta dawo a Arewa

An shafe aƙalla kwanaki 10 babu wutar lantarki a jihohin Arewacin Nijeriya.

Wutar Lantarki ta dawo a Arewa

Rahotanni sun bayyana cewa wutar lantarki da a bayan nan ta yi nisan kiwo ta dawo a wasu jihohin Arewacin Nijeriya.

Aminiya ta ruwaito cewa, an samu wutar lantarkin da yammacin wannan Larabar a jihohin Filato da Bauchi da Gombe da kuma Benuwe.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, mazauna birnin Jos da ke Jihar Filato sun shiga sowa da farin cikin bayan dawo da wutar lantarkin da misalin ƙarfe 7:20 na yammacin wannan Larabar.

Bayanai sun ce an shafe aƙalla kwanaki 10 babu wutar lantarki a jihohin Arewa da dama, lamarin da ya tsayar da harkokin kasuwanci bayan katsewar tashar samar da wutar lantarki da ke jihohin Benuwe da Enugu.

 

 

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta

Sojoji sun daƙile yunƙurin mayaƙan ISWAP a Borno