Ya bukaci ’yan sanda su daure shi don kubuta daga matarsa a gida

A cewarsa, rayuwar gida ta zamar mishi tamkar jahannama, so yake yi a kai shi gidan yari

Ya bukaci ’yan sanda su daure shi don kubuta daga matarsa a gida

Gidan yari

Wani magidanci da ke zaman takura a gida a Italiya ya gabatar da kansa a barikin ’yan sanda, inda ya bukaci a sakaya shi a cikin sel (dakin ajiye masu laifi) saboda takurar da yake fuskanta daga matarsa a gida wadda ya kasa jurewa, kamar yadda daya daga cikin jami’an ’yan sanda ya bayyana wa manema labarai.

Magidancin dan asalin kasar Albaniya mai shekara 30 da ke zaune a garin Guidonia Montecelio, a birnin Rome a kasar Italiya, “Ba ya iya jurewa kan tilasta kansa zama tare da matarsa,” kamar yadda wata sanarwa da wani dan sandan Carabinieri daga birnin Tivoli da ke makwabtaka da mutumin ya bayar.

’Yan sandan yankin sun fitar da bayanin cewa, “Abin da ya fusata magidanci game da lamarinshi ne, ya gwammace ya tsere wa matar daga gidan, hakan ya sa ya gabatar da kansa ga jami’an Carabinieri don neman a sakaya shi a dakin masu jiran hukunci bayan aikata laifi.”

Jami’an ’yan sandan sun rubuta cewa, “Mutumin ya kasance a tsare a gidan ne, saboda samun shi da laifukan ta’ammali da miyagun kwayoyi na wasu watanni kuma yana da shekaru kadan a gurfanar da shi,” a wani jawabi da Kyaftin Francesco Giacomo Ferrante na birnin Tivoli Carabinieri ya shaida wa Kafar Labarai ta AFP.

“Yana zaune a gida tare da matarsa da iyalansa. Hakan dai bai yi kyau ba,” inji Ferrante.

Magidancin ya ce, “Saurara, rayuwar gida ta zamar min tamkar jahannama, ba zan iya kuma zama a gidan ba, ni so nake yi a kai ni gidan yari.”

Nan take aka kama mutumin saboda saba dokar zamansa a gidansa da ya aikata, hukumomin shari’a sun ba da umarnin a kai shi gidan yari.

Zaɓen Edo: Yadda aka kama masu sayen ƙuri’a da ’yan daba

Sarakunan Nijar sun kai wa Gwamnatin Yobe ziyarar jaje

Ɗan majalisa ya yi jinjina kan naɗa Danyaya Sarkin Ningi

’Yan Sanda sun kama gungun ’yan fashi 7 a Katsina