Ya dace Kwankwaso ya rika tura masu horarwa waje kamar yadda yake tura dalibai -Mustapa Umar Tallo

Mai horar da  ’yan  wasan kwallon kafa na “ Gwarzo  Kwankwasiyya  Babes”, Mustapha Umar Tallo ya yi kira ga Gwamnan Jihar Kano Dokta Rabi’u Musa Kwankwaso  da ya  rika tura  masu horar da ’yan wasa na kulob-kulob da ke jihar kasashen ketare don kara masu kwarewa kamar yadda yake tura dalibai zuwa kasashen duniya don […]

Ya dace Kwankwaso ya rika tura masu horarwa waje kamar yadda yake tura dalibai -Mustapa Umar Tallo
Ya dace Kwankwaso ya rika tura masu horarwa waje kamar yadda yake tura dalibai -Mustapa Umar Tallo

Mai horar da  ’yan  wasan kwallon kafa na “ Gwarzo  Kwankwasiyya  Babes”, Mustapha Umar Tallo ya yi kira ga Gwamnan Jihar Kano Dokta Rabi’u Musa Kwankwaso  da ya  rika tura  masu horar da ’yan wasa na kulob-kulob da ke jihar kasashen ketare don kara masu kwarewa kamar yadda yake tura dalibai zuwa kasashen duniya don karo ilimi.
Malam  Mustapha Tallo Gwarzo yayi wannan kira ne a tattaunawar da ya yi da Aminiya dangane da  kwazon da kungiyoyin kwallon kafa na kananan hukumomin  Jihar Kano ke yi  musamman a harkar gasannin da  ake shiryawa lokaci zuwa lokaci.
Ya ce ko shakka babu Gwamna Kwankwaso yana kokari wajen  karawa matasa kwarin gwiwa  ta hanyar  wasannin kwallon kafa, wanda a cewarsa hakan ya taimaka  wajen hada kan matasa da sauran al’umma masu sha’awar wasan kwallon kafa a fadin jihar.
Tallo ya kara da cewa idan ana tura masu horar da ’yan wasa kasashen waje ko shakka babu za a sami kwararru wadanda za su kara fitar da jihar  kunya a kowace irin gasa da aka shirya walau a cikin gida ko wasu sassa na duniya.
Malam Mustapha Umar Tallo ya kuma jaddada cewa gwamnan Jihar Kano ya kasance zakara ta fannin kyautata yanayin wasannin motsa jiki  musamman kwallon kafa ta hanyar baiwa ’yan wasa da masu horar da su kyaututtuka masu karfafa gwuiwa.
Ya yi amfani da wannan dama wajen yin tuni ga Gwamna Kwankwaso a bisa alkawarin da ya yi na tallafawa kungiyoyin kwallon kafa da aka zaba daga kananan hukumomomi wadanda har yanzu ba cika musu wannan alkawari ba.
A karshe, Malam Mustapha Umar Tallo Gwarzo ya yi kira ga  matasan Jihar Kano su ci gaba da kasancewa  masu bin doka da son zaman lafiya ta yadda  zamantakewa za ta kara inganta sannan ya hori kungiyoyin kwallon kafa na jihar  su kara zage damtse wajen ganin sun kasance zakaru a harkar kwallon kafa.