Ya lakadawa matarsa duka ta mutu a Ogun
Hukumar ‘yan sandan jihar Ogun ta kama wani mai suna Shina Kasali dan shekara 38 wanda ya lakadawa matsarsa duka ta mutu. Lamarin ya faru ne a yankin Abosule da ke unguwar Agbado ta karamar hukumar Ifo a jihar. Wani makwabcin ma’auratan ne ya sanarwa ofishin ‘yan sandan Agbado. Kakakin hukumar ‘yan sandan Abimbola Oyeyemi […]
Hukumar ‘yan sandan jihar Ogun ta kama wani mai suna Shina Kasali dan shekara 38 wanda ya lakadawa matsarsa duka ta mutu.
Lamarin ya faru ne a yankin Abosule da ke unguwar Agbado ta karamar hukumar Ifo a jihar. Wani makwabcin ma’auratan ne ya sanarwa ofishin ‘yan sandan Agbado.
Kakakin hukumar ‘yan sandan Abimbola Oyeyemi ya ce, an samu rashin jituwa tsakanin ma’auratan ne lokacin matar mai suna Sofiyat ta yi yunkurin fita iban ruwa amma mijin nata ya ki yarda.