Ya rasu a yayin buɗa-baki a Abuja
Wani mutum wanda aka bayyana a matsayin Abdulrashid Usman, ya yanke jiki ya mutu a yayin da yake buɗa-baki a yankin Babban Birnin Tarayya.

Gawa
Wani mutum wanda aka bayyana a matsayin Abdulrashid Usman, ya yanke jiki ya mutu a yayin da yake buɗa-baki a yankin Babban Birnin Tarayya.
Wani shaida mai suna Suleiman Bala, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar da aka ɗauki azumi, lokacin da mamacin da abokansa suke buɗe-baki a majalisarsu da ke yankin Kutunu a Ƙaramar Hukumar Gwagwalada.
Ya ce Usman da abokansa suna zaune a kan benci suna cin ’ya’yan itatuwa ne ya yanke jiki ya faɗi, rai ya yi halinsa.
Nan take abokan suka garzaya da shi zuwa asibiti, inda likita ya tabbatar cewa rai ya yi halinsa.
A cewarsa, marigayin, wanda yake cikin koshin lafiya, ya dawo daga Kaduna ganin buɗa-baki, daga nan ya je majalisarsu ya haɗu da abokansa, bayan an sha ruwa suna tsaka da buɗa-baki lamarin ya faru.
“Wani ɗan uwan marigayin ya ce mamacin ya dawo daga Kaduna kuma ya je shiga cikin abokansa inda suke annashuwa.
“Bayan kiran Sallah suna buɗa-baki lamarin ya faru,” in ji shaidar.
Ya ce an binne shi bisa tsarin addinin Musulunci.