Yadda Jam’iyyar PDP Ta Fada Tsaka Mai Wuya

Kwamitin Amintattun PDP zai zauna don bitar guguwar da ke neman kai jam’iyyar kasa.

Yadda Jam’iyyar PDP Ta Fada Tsaka Mai Wuya

Uche Secondus, Shugaban Jam’iyyar PDP na Kasa

Ranar Alhamis 5 ga watan Agusta Kwamitin Amintattu na PDP zai yi wani taro a Abuja don bitar guguwar da ke neman kai babbar jam’iyyar adawar ta Najeriya kasa.

Taron dai ya biyo bayan ajiye aiki ne da wasu shugabannin jam’iyyar na kasa su bakwai suka yi a farkon mako.

Shirin Najeriya a Yau ya duba a kan wannan lamari don gano yadda aka yi aka haihu a ragaya.