Yadda Jam’iyyar PDP Ta Fada Tsaka Mai Wuya
Kwamitin Amintattun PDP zai zauna don bitar guguwar da ke neman kai jam’iyyar kasa.
Uche Secondus, Shugaban Jam’iyyar PDP na Kasa
Ranar Alhamis 5 ga watan Agusta Kwamitin Amintattu na PDP zai yi wani taro a Abuja don bitar guguwar da ke neman kai babbar jam’iyyar adawar ta Najeriya kasa.
Taron dai ya biyo bayan ajiye aiki ne da wasu shugabannin jam’iyyar na kasa su bakwai suka yi a farkon mako.
Shirin Najeriya a Yau ya duba a kan wannan lamari don gano yadda aka yi aka haihu a ragaya.