Yadda mata ta haihu a kan hanya a Zariya

Wata mata da ake zato mara lafiya ce ta haihu a wani rusasshen kango da ke gefen hanya a Zariya. Wani likita da ke hanyarsa ta zuwa Samaru, Dokta Mustapha Muhammad ne ya ba wa mai jegon wadda ba a san daga inda ta fito ba kulawar gaggawa. Budurwa ta rataye kanta a Kano Yadda […]

Yadda mata ta haihu a kan hanya a Zariya

Wata mata da ake zato mara lafiya ce ta haihu a wani rusasshen kango da ke gefen hanya a Zariya.

Wani likita da ke hanyarsa ta zuwa Samaru, Dokta Mustapha Muhammad ne ya ba wa mai jegon wadda ba a san daga inda ta fito ba kulawar gaggawa.

“Matar ta haihu lafiya sai dai mahaifarta ba ta fita ba kuma ka san tunda ba yadda ta iya don haka sai ta dauki dan ta rungume, ka ji yadda aka yi, amma yanzu Allah Ya sa mahaifar ta fita kuma na yanke cibiyar”, inji shi.

Kangon da matar ta haihu na daura da ofishin Hukumar Kula da Kiyaye Handura ta Kasa (FRSC) a titin da ya tashi daga PZ zuwa Samaru, Karamar Hukumar Sabon Gari, Jihar Kaduna.

Daga baya Jami’an FRSC sun dauki matar a motarsu zuwa Sashen Kula da Walwala da Jin Dadi na karamar hukumar domin ci gaba da lura da ita.

Ya Kamata A Hanzarta Aikin Hako Man Kolmani

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 8, sun ceto mutum 16

APC ta lashe duk kujerun kananan hukumomi a zaben Sakkwato

Sojoji sun kama ’Yan Yahoo 150 a kusa da bariki a Delta