Yadda Mataimakin Shugaban Majalisar Nasarawa ya yi hatsari

Hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10 na safe, a lokacin da Mataimakin Shugaban Majalisar ke taka da tafiya a cikin motar. 

Yadda Mataimakin Shugaban Majalisar Nasarawa ya yi hatsari

Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa, Rt. Hon. Muhammad Adamu Oyanki, ya tsallake rijiya da baya a wani mummunan hatsarin mota a ranar Litinin a kan hanyar Keffi-Akwanga.

Hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10 na safe, a lokacin da Mataimakin Shugaban Majalisar ke taka da tafiya a cikin motar.

Daga bisani aka ɗauke motar da ta lalace zuwa harabar majalisar da ke Lafia.

A ranar Litinin, Shugaban Majalisar, Rt. Hon. Dr. Danladi Jatau, tare da wasu ’yan majalisa, sun duba motar da ta lalace a harabar majalisar.

Jatau ya bayyana lamarin a matsayin abin baƙin ciki, sai dai ya gode wa Allah da babu wanda ya rasa ransa a hatsarin.

“Mun gode wa Allah Maɗaukaki da ya tsare rayuwar Mataimakin Shugaban Majalisar daga wannan hatsarin mota. Muna farin cikin cewa yana raye kuma lafiya,” in ji shi.

Wakilinmu ya gano cewa Mataimakin Shugaban Majalisar yana cikin ƙoshin lafiya a halin yanzu.