Yadda za a duba sakamakon jarabawar JAMB

Matakan da za ku bi domin samun sakamakon jarabawar cikin sauki.

Yadda za a duba sakamakon jarabawar JAMB

Dalibai na zana jarabawar JAMB

Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta fitar da sakamakon jarabawar (UTME) da aka zana ranar 3 ga Yuni, 2021.

An gudanar da jarabawar a dukkanin cibiyoyin da aka ware na CBT a fadin kasar nan.

  1. Yadda Pogba ya cire kwalbar giya a gabansa
  2. Mun gano Ministar da ta sayi kadarar Dala miliyan 37 a boye — EFCC

Wata sanarwa da mai magana da yawun JAMB din, Dokta Fabian Benjamin, ya fitar a ranar Laraba, ta ce sakamakon mutum 62,780 ne ya fito daga cikin dalibai 160,718 da suka zauna jarabawar.

Ga matakan da za a bi don duba sakamakon jarabawar:

  • Ziyarci shafin JAMB a https://jamb.gov.ng/efacility
  • Shiga “UTME 2021 Mock Results Notification Slip”
  • A ciki za a ga inda za a sa lambar jarabawar.
  • Idan aka sa lambar a wajen aai a danna neman sakamakon jarabawa.
  • Sai a jiya, bayan dakikoki sakamakon zai bayyana.

Kazalika, za a iya duba sakamakon jarabawar ta wannan hanya:

  1. Shiga shafin JAMB a jamb.gov.ng
  2. Saka adireshin email da lambobin sirrin da aka yi amfani da su yayin rajistar UTME 2021.
  3. Sai a danna nemo sakamako.
  4. Sakamakon jarabawar zai bayyana cikin PDF, sai a fitar da shi.

A-Kurkura: Guba ko Magani?

Tsohon Shugaban Jami’ar Ilori, Farfesa Ambali ya rasu

ICPC ta hana El-Rufai ganin likita —Hadiminsa

Hanyoyin zuwa Katsina sun zama tarkon mutuwa