Yadda Zulum ya halarci jana’izar manoma 43 da aka yi wa yankan Rago

Gwamnan ya halarci sallar jana’izar da aka yi inda ya taimaka wajen birne manoma 43.

Yadda Zulum ya halarci jana’izar manoma 43 da aka yi wa yankan Rago

Zulum yana taimakawa wajen ajiye gawa

A ranar Lahadi, Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya halarci sallar jana’izar manoma 43 da mayakan Boko Haram suka yi wa yankan Rago.

Aminiya ta ruwaito cewa a Asabar din da ta gabata ne mayakan suka yi wa akalla manoma 40 dirar mikiya a gonaki, suka daddaure su, suna yankawa a kauyen Koshobe, da ke Zabarmari, Karamar Hukumar Jere.

Gwamna Zulum yayin da ake sallar jana’iza
Zulum yana taimakawa wajen ajiye gawa
Gawarwakin Mutane 43 da aka yiwa yankan Rago
Gawarwakin Mutane 43 da aka yiwa yankan Rago

 

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta