’Yan ɗaurin aure 19 daga Kano sun rasu a hatsarin mota a Filato

Mutum 11 daga cikinsu sun tsallaka rijiya da baya da raunuka a haɗarin da ya ritsa da su a yayin da suke hanyar komawa gida bayan ɗaurin auren da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Barikin Ladi a ranar Asabar.

’Yan ɗaurin aure 19 daga Kano sun rasu a hatsarin mota a Filato

Wani hatsarin mota da ya faru a Bauchi (tsohuwar ajiya)

Mahalarta ɗaurin aure mutum 19 daga Jihar Kano sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota a yankin Kwanar Maciji da ke Ƙaramar Hukumar Pankshin a Jihar Filato.

Mutum 11 daga cikinsu sun tsallaka rijiya da baya da raunuka a haɗarin da ya ritsa da su a yayin da suke hanyar komawa gida bayan ɗaurin auren da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Barikin Ladi a ranar Asabar.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Pankshin, John Dasar, ya bayyana cewa motar matafiyan ta kama da wuta ne, amma an yi nasarar ceto direban da wasu fasinjoji.

Ya ce, “an ceto mutane 11 amma mutane 19 sun kone ƙurmus ba za a iya gane su ba, saboda bayan mutane sun zo ana ƙoƙarin ceto fasinjojin ne motar ta kama da wuta, ta cinye ragowar.”

Ya ce an kai waɗanda suka tsira Babban Asibitin Pankshin inda ake duba lafiyarsu.

Majalisar wakilai ta dakatar da CBN daga ƙara kuɗin cajin ATM

Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

’Yan sanda sun ceto mutum 30 daga hannun ’yan bindiga a Katsina

Ba abin da zai faru idan aka tsige Fubara – Wike