‘Yan ta’adda sun harbe wani mutum a Kano

‘Yan bindigar sun tsere da motar mutumin, bayan sun harbe shi a kirji.

‘Yan ta’adda sun harbe wani mutum a Kano

Wasu ’yan ta’adda sun harbe wani mutum a birnin Kano daura da babban kantin nan na Ado Bayero Mall da ke kan titin gidan Zoo.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kano, DSP Haruna Abdullahi Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin wanda a cewarsa ya auku ne a daren ranar Asabar.

DSP Kiyawa ya ce ’yan bindigar sun harbe Alhaji Isah Abubakar, kuma da jin sautin harbin ne jami’ansu suka isa wurin.

Ya ce an garzaya da mutumin zuwa asibiti inda a nan rai ya yi masa halinsa.

Wani wanda lamarin ya faru a kan idonsa ya shaidawa Aminiya cewa, “sun yi kokarin fito da shi daga motarsa, inda bayan ya yi musu tirjiya suka harbe shi a kirji,” in ji sa.

Ya ce bayan ’yan bindigar sun harbe shi sun kuma rika harbe-harbe cikin isa gabanin su tsere da motarsa inda suka bar shi kwance yana ta zubar jini a gefen hanya.

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta

Sojoji sun daƙile yunƙurin mayaƙan ISWAP a Borno