’Yan bindiga sun harbi fasinjoji 2, sun sace makiyaya a Neja
Maharan sun kuma sace wasu makiyaya.
’Yan bindiga sun kai wa wata mota hari a kan hanyar Tegina zuwa Kontagora a Jihar Neja, inda suka jikkata mutum biyu.
Harin ya faru ne a Tudun-Fulani bayan direban motar ya ƙi tsayawa lokacin da ’yan bindigar suka buƙaci ya tsaya.
- ’Yan Najeriya sun kusa fara shan wutar sa’o’i 24 babu ɗaukewa — Minista
- Jonathan ya tattauna da Peter Obi kan tsayawa takara a 2027
Rashin tsayawarsa ya sa maharan suka buɗe wa motar wuta, inda suka jikkata fasinjoji biyu da ke zaune a kujerar gaba.
Wannan lamarin ya faru ne bayan sa’o’i da ’yan bindigar suka sace wasu makiyaya a garin Usalle da daren ranar Laraba.
Rahotanni sun nuna cewar ’yan bindigar sun tura makiyayan bakin hanya sannan suka yi yunƙurin amfani da su wajen tare motocin da ke wucewa a kusa da ƙauyen Samaza Sauri da ke Ƙaramar Hukumar Kontagora.
Wani mutum ya ce: “Da misalin ƙarfe 10:30 na dare, sun sace wasu makiyaya a Usalle.
“Bayan nan suka tare hanya a Samaza Sauri, sun buɗe wa motoci da ke zuwa Kontagora wuta, inda suka jikkata mutum biyu a ƙafafunsu.”
Rundunar ’Yan sandan Jihar Neja, ta tabbatar da aukuwar harin.
Kakakin rundunar, SP Wasiu Abiodun, ya ce: “A ranar 11/09/2025 da misalin ƙarfe 12:15 na dare, wasu ’yan bindiga sun yi ƙoƙarin tare wata mota a Tudun-Fulani.
“Direban ya tsere, amma sun buɗe musu wuta tare da jikkata fasinjoji biyu. An kai su asibiti, amma ba a sace kowa ba.”
’Yan sanda da jami’an tsaro sun isa wajen da harin ya auku, amma ’yan bindigar sun tsere cikin daji.
A wani harin kuma, ’yan bindiga sun shiga ƙauyukan Uzange da Matachibu a gundumar Masuga da ke Ƙaramar Hukumar Kontagora, inda suka sace mutum uku cikin daren ranar Alhamis.
Mazauna Ƙananan Hukumomin Kontagora, Mariga, da Magama, sun bayyana cewa hare-haren ’yan bindiga sun ƙaru a baya-bayan nan, inda suka ce an sace mutane da dama tare da yin awon gaba da ɗaruruwan shanu.