’Yan bindiga sun sace DPO a Kaduna

DPO din na kan hanyarsa ta zuwa Birnin Gwari ne domin kama sabon aikinsa.

’Yan bindiga sun sace DPO a Kaduna

Jami’in dan sanda

’Yan bindiga sun yi awon gaba da wani DPO din ‘yan sanda da aka tura aiki kwanan nan zuwa Birnin Gwari a Jihar Kaduna.

An sace DPO din ne a hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari da misalin karfe 9 na safe a ranar Litinin.

Majiyoyi sun shaida wa Aminiya cewa DPO din na kan hanyarsa ta zuwa Birnin Gwari ne domin kama sabon aikinsa a lokacin da lamarin ya faru.

Sai dai kawo yanzu babu tabbaci ko jami’in na tafiya ne shi kadai a cikin motar lokacin da aka dauke shi ba.

Har yanzu dai ’yan sanda ba su ce uffan ba ballantana fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

Da aka tuntubi Mohammed Jalinge, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna, ya ce, “Zan binciko lamarin tukunna.”