‘Yan bindiga sun sace tsohowa mai shekara 90 a Zamfara

‘Yan bindigar sun yi awon gaba da tsohuwa mai shekara 90 a Karamar Hukumar Kauran Namoda a jihar Zamfara.

‘Yan bindiga sun sace tsohowa mai shekara 90 a Zamfara

Wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da wata tsohuwa mai shekara 90 a garin Kurya Madaro dake Karamar Hukumar Kauran Namoda a jihar Zamfara.

Wata majiya a kauyen ta ce, bayan tsohuwar da aka dauke, sun kuma tafi da wasu matasa hudu wanda biyu daga cikinsu yan gida daya ne.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar sun afkawa garin ne da misalin karfe 12 na daren asabar inda suka yi awon gaba da tsohuwar mai suna Hajiya Aisha bayan da suka gaza kama danta, Alhaji Danbaba, wanda dan kasuwa ne.

“Dan ta suka zo nema, da basu same shi ba dai suka dauki mahaifiyarsa da ba ta iya ko tafiya saboda tsufa,” inji majiyar.

Kokarin jin ta bakin Kakakin Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar, SP Muhammad Shehu ya ci tura, saboda rashin samunsa a waya har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta